Shugaban kasar Turkiyya Rajab Tayyib Erdugan ne ya kirayi zaman taron gaggawa na shugabannin kasashen kungiyar hadin kan kasashen musulmi ta O.I.C domin tattauna batun hare-haren wuce gona da iri da gwamnatin haramtacciyar kasar Isra'ila ke ci gaba da kai wa kan al'ummar Palasdinu musamman batun kisan kiyashi da ta yi wa Palasdinawa a yankin Zirin Gaza a ranar bude ofishin jakadancin Amurka a birnin Qudus.
Ana sa-ran shugabannin kasashen Musulmi fiye da 40 ne zasu halacci zaman taron gaggawan da za a gudanar a yau Juma'a a birnin Istambul na kasar ta Turkiyya.
18 Mayu 2018 - 12:50
Lambar labari: 893937
Shugaban kasar Iran ya kama hanyar tafiya zuwa kasar Turkiyya domin halattar zaman taron kungiyar hadin kan kasashen Musulmi ta O.I.C kan matsalar Palasdinu.